Yadda aka mayar da jaririyar da aka yi wa tiyata a zuciya fagen daga a Gaza

- Marubuci, Adnan El-Bursh
- Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC News Arabic Gaza reporter
Enas Abu Daqqa ce zaune cikin tantinsu a sansanin 'yan gudun hijira da ke al-Shati da ke arewacin zirin Gaza, dauke da 'yarta Naveen, ga wata fanka da ke taimakawa wajen rage zafin da ake fama da shi a safiyar.
Hankalin Enas ba a kwance ya ke ba, ta damu kan halin da 'yarta Naveen ke ciki na rashin lafiya. Watannin ta 6, an kuma haife ta ana tsaka da yaki da kuma rami a zuciyarta.
Kamar yadda ta bayyana, ta na fadi tashin ganin 'yarta ta rayu a daidai lokacin da fannin lafiya ke kara tabarbarewa a Gaza. Naveen ta tsanyara kuka idanunta masu launin ruwan kasa sun firfito alamar da ke nuna tsananin rashin lafiya.
"Yakin nan mai tsanani ne a gare ta," kamar yadda Enas ta shaidawa BBC. "Ba ta girma, ba ta da nauyi, kuma kowanne lokaci za ta iya fara rashin lafiya."
Damar da ake da ita. domin ceton Niveen, shi ne a bata kulawar gaggawa a wajen Gaza. Kuma afarkon watan Maris kasar Jordan ta tabbatar da hakan.
Lokacin da aka cimma tsagaita wuta tsakanin Isra'ila da Hamas, an samu damar fitar da yara 29 da ke bukatar kulawar gaggawa kuma Naveen na daga cikinsu, an kai su asibiti a kasar Jordan. Mahaifiyarta da 'yayarta na daga cikin wadanda sukai mata rakiya.
Su ne yara na farko da aka kai Jordan, bayan Sarki Abdullah ya sanar da shirin yi wa yara 2,000 da ke tsananin bukatar kulawar likita daga Gaza zuwa asibitocin Jordan. An yi aikin ne da hadin gwiwar hukumomin Isra'ila da sukai bincike kan iyayen yaran da su kan su yaran.
Likitoci a Jordan sun yi nasarar yi wa Naveen tiyata, kuma sannu a hankali ta na murmurewa.
Sai dai makonni biyu bayan hakan, yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ta rushe, hakan na nufin an koma yaki fiye da lokutan baya. Enas ta shafe makonni ta na kallon abin da ke faruwa a Gaza, ta akwatin talbijin din dakin asibitin da suke a Jordan, ta shiga damuwa kan halin da mijinta da sauran 'ya'yanta ke ciki a gida.
Kwatsam a daren ranar 12 ga watan Mayu, hukumomin Jordan suka shaidawa Enas za a maida su Gaza a wanshekare, a cewarsu Naveen an kammala aikin da aka yi wa Naveen.
Lamarin ya kada Eanas.
"Mun baro Gaza lokacin an tsagaita wuta. Ta yaya za ku maida mu yanzu da ake tsaka da yaki");