window.__reverb = {}; window.__reverb.__reverbLoadedPromise = new Promise((resolve, reject) => { window.__reverb.__resolveReverbLoaded = resolve; window.__reverb.__rejectReverbLoaded = reject; }); window.__reverb.__reverbTimeout = setTimeout(() => { window.__reverb.__rejectReverbLoaded(); }, 5000);

Mutum sama da miliyan daya sun kamu da coronavirus a duniya

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a duniya baki daya dangane da annobar coronavirus.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya, Awwal Ahmad Janyau, Usman Minjibir and Umar Mikail

  1. An fara zaman gida a Eritrea saboda coronavirus

    Kasar Eritrea ta saka dokar zaman gida na tsawon kwana 21 domin dakile yaduwar coronavirus.

    Sanarwar ta zo ne bayan ministan lafiya ya bayar da rahoton karin mutum uku da suka kamu da cutar, abin da ya kawo adadin wadanda suka kamu a kasar zuwa 18.

    Daya daga cikinsu yarinya ce 'yar shekara 13, wadda ta harbu da cutar daga mahaifiyarta wadda ta koma daga kasar waje.

    Su ma sauran biyun sun koma kasar ne kafin a haramta saukar jiragen haya a kasar, a cewar ma'aikatar lafiya.

    Yayin dokar, dukkanin 'yan kasar wadda ke bin tsarin jam'iyyar siyasa guda daya sannan take da nuna karfin soja, za su kasance a gida - ma'aikata da 'yan kasuwa.

    Mutum daya daga kowane gida yana da damar fita domin sayen kayan abinci da rana a shagunan cefane, wadanda za su kasance a bude.

    Su ma kantinan sayar da magani da bankuna za su ci gaba da kasancewa a bude, amma an rufe kasuwanni na mako-mako da sauran wuraren kasuwanci.

    Sai dai manoma da ke zaune a yankunan karkara ba sa cikin wannan doka sakamakon abinci da suke samarwa.

    Ayyukan gine-gine ma za su ci gaba da gudana, kamar yadda ma'aikatar lafiya ta bayyana.

    An rufe kasuwanni irin wadannan yayin zaman ngidan

    Asalin hoton, Getty Images

  2. Coronavirus: 'Yan Najeriya za su rika kallon tashoshin talabijin kyauta a DSTV da StarTimes

    Bajon gidan talabijin na NTA

    Asalin hoton, NTA

    Hukumar da ke sa ido kan kafofin yada labarai a Najeriya wato National Broadcasting Commission (NBC) ta umarci masu samar da layin kallon tashoshin talabijin su kyale 'yan Najeriya su kalli tashoshin cikin gida kyauta.

    Mininstan Yada Labarai na Najeriya, Lai Mohammed ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a wurin taron manema labarai na kullum-kullum da kwamitin musamman kan yaki da coronavirus ke gudanarwa.

    Ya ce an dauki matakin ne saboda a tabbatar da cewa 'yan Najeriya sun samu cikakkun bayanan da suka kamata a kan annobar coronavirus, wadda ke haddasa cutar Covid-19.

    Ministan yana magana ne kan kamfanoni kamar DSTV da kuma StarTimes, wadanda su ne ke samar da ma fi yawan layukan da ake amfani da su na kallon tashoshin talabijin ta hanyar tauraron dan Adam.

    "Yadda abin yake shi ne, idan kuka sayi katin DSTV ko StarTimes kuma kudinku ya kare to za ku iya ci gaba da kallon tashoshin NTA da Channels da TVC da AIT da sauransu," in ji Lai Mohammed.

    Zuwa yanzu mutum 174 ne suka kamu da coronavirus a Najeriya, yayin da tara daga cikinsu suka warke sannan kuma biyu suka mutu, a cewar hukumar NCDC mai yaki da yaduwar cutuka a kasar.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  3. Masana sun soma gwajin riga-kafin coronavirus

    Masana kimiyya

    Asalin hoton, CSIRO

    Masana kimiyya a Australia sun soma gwajin riga-kafin cutar coronavirus guda biyu a wani "gagarumin" mataki da suka kaddamar a dakin gwaje-gwaje.

    Tuni Hukumar Lafiya ta Duniya ta amince Jami'ar Oxford da wani kamfanin magunguna na Amurka Inovio Pharmaceutical su soma gwajin maganin riga-kafin.

    Hukumar kimiyya ta Australia za ta sanya ido kan ko riga-kafin zai yi amfani ko kuma idan dan adam zai iya amfani da shi.

    An soma gwajin farko na riga-kafin ne a Amurka a watan jiya, ko da yake ba a gwada shi a kan dabbobi ba.

    Ana gudanar da gwaje-gwaje da dama na riga-kafin coronavirus a fadin duniya cikin hanzari.

  4. Coronavirus: Bankin Duniya zai bai wa Kenya bashin $50m

    Kungiyar likitoci ta ce mambobinta na bukatar karin takunkuman fuska

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Kungiyar likitoci ta ce mambobinta na bukatar karin takunkuman fuska

    Kenya za ta karbi rancen dala miliyan 50 daga Bankin Duniya a kokarinta na hana yaduwar coronavirus.

    Ministan Lafiya Mutahi Kagwe ya ce za a yi amfani da kudin ne domin sayo takunkuman fuska ga ma'aikatan lafiya, da man wanke hannu wato hand sanitisers da kuma kara gadaje a asibitoci.

    Ma'aikatan lafiyar kasar sun koka kan rashin isassun takunkuman fuska a asibitoci, a cewar jaridar Daily Nation.

    Ma'aikatar Lafiya ta tabbatar da ma'aikacin lafiya guda daya da ya kamu da covid-19 - kafafen watsa labaran kasar suka ce ya kamu ne bayan ya yi mu'amala da wani mai dauke da cutar.

    Kungiyar likitoci ta ce mambobinta na bukatar karin takunkuman fuska sannan ta yi kira ga gwamnati ta samar da su a cikin gida.

    Macen farko da ta kamu da coronavirus a Kenya, wadda tuni ta warke, ta yaba wa ma'aikatan lafiyar da suka kula da ita, tana mai cewa sun yi kokari duk da kalubalen da suke fuskanta.

  5. An rufe Isra'ila saboda coronavirus

    Ana korafi a Isra'ila saboda jinkirin da mabiya darikar Orthodox

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Ana korafi a Isra'ila saboda jinkirin da mabiya darikar Orthodox ke yi na bin umarnin da gwamnati ta bayar

    An takaita zirga-zirga a garin Yahudawa mabiya darikar Orthodox da ke yammacin Isra'ila, inda ya kasance cibiyar coronavirus a kasar.

    'Yan sanda sun sanya shingaye a kusa da Bnei Barak da ke gefen birnin Tel Aviv, lamarin da ya takaita zirga-zirga sannan za a kai mutanen da aka killace otal-otal domin su zauna a can.

    Bnei Barak ne gari na biyu da aka fi fama da masu dauke da Covid-19 a kasar.

    Kazalika ana korafi a Isra'ila saboda jinkirin da mabiya darikar Orthodox ke yi na yin biyayya ga matakan kariya daga coronavirus da hukumomin lafiya suka zayyana.

  6. Covid-19: Wutar lantarki ta kashe mutum 20 a Congo

    Lantarki

    Asalin hoton, Getty Images

    Wasu mutum 20 sun rasa rayukansu bayan wasu manyan wayoyin wutar lantarki sun fado kansu a kasar Congo-Brazzaville, a cewar hukumomi.

    Lamarin ya faru ne a rana ta farko da aka fara zaman gida a babban birnin kasar Brazzaville domin kauce wa yaduwar annobar coronavirus.

    Zuwa yanzu mutum 22 ne suka kamu da cutar ta Covid-19 sannan biyu suka mutu a kasar.

    Shugabar garin Kintele, Stella Mensah Saddou Nguesso, ta ce wayoyin da suka fado ne suka yi ajalin mutanen.

    Wadanda suka shaida faruwar lamarin sun ce waya daya ta fado kan wani gida, inda nan take ya fara ci da wuta tare da kashe dukkanin wadanda suke cikinsa.

    Wata wayar kuma ta fada kan wani wurin linkaya a farfajiyar wani gida sannan ta yi wa makwabtansa shokin.

    An yi ta tafka ruwan sama a Kintele na tsawon sa'o'i.

    Mutane sun samu nasarar daukar wadanda suka ji rauni zuwa asibiti da kuma wadanda suka mutu a motocinsu sakamakon gawarwakin sun yi wa motocin asibiti yawa.

    Tasawira
  7. Ganduje da mai dakinsa 'ba sa dauke da coronavirus'

    Sakamakon gwajin coronavirus da aka yi wa gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje da mai dakinsa Hafsat ya nuna cewa ba sa dauke da cutar, in ji wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar.

    Sanarwar, wacce mai magana da yawun gwamnan, Abba Anwar, ya aikewa manema labarai ranar Alhamis a kara da cewa: "Mun gode wa Allah Madaukakin Sarki game da wannan sakamako da ya nuna cewa ba sa dauke da cutar.

    Za mu ci gaba da addu'ar neman sauki ga dukkan wadanda sakamakonsu ya nuna suna dauke da cutar. Ba tare da la'akari da kasarsu ko kabilarsu da jam'iyyar siyasarsu ko kuma addininsu ba."

    Ko da yake sanarwar bata fadi lokacin da aka yi wa gwamnan da mai dakinsa gwajin covid-19 ba, amma ta yi kira ga dukkan al'umma su bi umarnin masana harkokin lafiya wajen wanke hannayensu akai-akai da yin amfani da man goge hannu, wato hand sanitizer da kuma tsaftace muhallinsu.

    "Ku guji zuwa wurin taruwar jama'a musamman kasuwanni da sauran wuraren haduwar jama'a... Zama a gidajenku shi ne ya fi alheri," in ji Gwamna Ganduje.

    Gwamnan ya bi sahun wasu gwamnoni, irin su gwamnan Naija, Abubakar Sani Bello; gwamnan Kebbi, Atiku Badugu da sauransu, wadanda suka ce ba sa dauke da cutar bayan gwajin da suka yi.

    Sai dai gwamnoni irin su Bala Mohammed na Bauchi, Nasir El-Rufai na Kaduna da Seyi Makinde na Oyo, sun bayyana cewa suna dauke da cutar kuma sun killace kansu inda suke karbar magani.

    Ganduje

    Asalin hoton, ALAMY

    Bayanan hoto, Ganduje ya yi addu'a ga masu dauke da coronavirus
  8. Hukumar Lafiya ta Duniya ta bukaci gwamnatoci su ba talakawa abinci

    Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO, Mr Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya yi kira ga gwamnatoci su bai wa talakawa abinci domin rage radadin da suke ciki sakamakon hana su fita daga gidajensu.

    Kasashe da dama sun dauki matakai daban-daban a kokarin hana yaduwar coronavirus, ciki har da umartar mutane su zauna a gidajensu.

    Hakan ne ya sa akasarin talakawa suke kokawa kan wannan mataki, ko da yake gwamnatoci da dama sun bullo da tsarin bai wa marasa galihu abinci.

    Sai dai Mr Ghebreyesus ya wallafa sako a Twitter ranar Alhamis, inda ya ce ko da yake rufe kasashe da hana mutane fita daga gidajensu yana iya rage yaduwar covid-19, wadannan matakai za su iya yin mummunar illa ga talakawa da marasa galihu.

    "Ina kira ga kasashe su tabbatar cewa wadannan mutane [talakawa da marasa galihu] sun samu abinci da sauran kayan bukatu a wannan mawuyacin hali," in ji Mr Ghebreyesus

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  9. Fiye da mutum 194,000 sun warke daga coronavirus

    Alkaluman da ke fitowa daga Jami'ar Johns Hopkins ta Amurka, wacce ke bibiyar halin da ake ciki game da coronavirus, sun nuna cewa akalla mutum 194,000 sun warke daga cutar ya zuwa safiyar ranar Alhamis, 2 ga watan Afrilu, 2020.

    A cewar Jami'ar, sama da mutum 938,000 ne suka kamu da cutar a fadin duniya, yayin da fiye da mutum 47, 000 suka mutu.

    Kasashe goman da suka fi fama da annobar su ne:

    Amurka – 216,722

    Italiya – 110, 574

    Spaniya – 104, 118

    China - 82,394

    Jamus - 77, 981

    Faransa - 57, 763

    Iran - 47,593

    Birtaniya - 29,865

    Switzerland – 17,768

    Turkiyya - 15,679

  10. Budewa,

    Nasidi Adamu Yahaya ne yake yi muku barka da wannan safiya. Da fatan za ku kasance tare da mu domin sanin halin da duniya ke ciki dangane da coronavirus, cutar da ta addabi kasashen duniya.

    Baya ga lamarin wannan cuta, za kuma mu kawo muku sauran labarai da rahotannin da suka shafi rayuwarku, musamman daga kasashen Najeriya da Nijar da ma sassan duniya.

    Kuna iya tafka muhawara da bayyana ra’ayoyinku a shafukanmu na sada zumunta a BBC Hausa.

  11. Rufewa

    To masu bibiyarmu nan muka zo karshen wannan shiri. Sai kuma gobe Alhamis da safe inda za mu ci gaba da kawo muku bayanai kai tsaye dangane da halin da Najeriya da duniya ke ciki kan annobar coronavirus. Da fatan Allah ya ba mu alkairinsa. Sai da safe.

  12. Coronavirus: 'Masu cutar HIV na bukatar kulawa ta musamman'

    Hukumar da ke yaki da cuta mai karya garkuwar ji ko SIDA a Najeriya na nuna damuwa dangane da hadarin da masu cutar ke fuskanta a wannan yanayi na annobar coronavirus.

    Shugaban hukumar a Najeriya, Dr Gambo Aliyu ya ce dole ne a kula da rayuwar masu dauke da cutar musamman wadanda dauke da cutar HIV amma ba su sani ba.

    Ya ce wadanda ba su san suna dauke da cutar ta HIV ba a kasar sun kai akalla fiye mutum dubu 500.

    Dr Gambo Aliyu ya ce masu cutar SIDA na bukatar taimako saboda raunin da suke fama da shi na garkuwar jiki.

    HIV

    Asalin hoton, Getty Images

  13. Coronavirus: PDP na son a sa ido kan gudunmowar da jama'a ke bayarwa

    pdp

    Asalin hoton, PDP

    Babbar Jam’iyyar adawa ta PDP ta ce ta yi kira ga shugaban kasar Muhammadu Buhari da ya kafa wani kwamiti da zai rika lura da kudaden tallafin da daidaikun mutane da kamfanoni masu zaman kansu ke bai wa kasar na yaki da Coronavirus.

    Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar, ta na cewa ta nemi hakan ne domin tabbatar da kudaden da ake bayarwa sun je hannun wadanda aka bayar domin su ta bangaren kiwon lafiya da tattalin arziki a fadin kasar.

    Jam’iyyar ta PDP ta ce kamata ya yi kwamitin kar-ta-kwana kan Covid-19 da shugaban kasa ya kafa ya tsame hannunsa daga kan wadannan kudaden tallafi domin kauce wa cin hanci da rashawa da kuma siyasantar da su.

  14. Filato za ta rufe iyakokinta daga Alhamis

    Gwamnatin jihar Filato ta ce za ta rufe dukkanin kofofin shiga jihar domin dakile cutar coronavirus daga jihar.

    Wata sanarwa da kwamishinan yada labaran jihar Dan Manjang ya fitar ta ce matakin zai fara aiki ne daga karfe shida na safiyar Alhamis ranar 2 ga Afrilu.

    Sanarwar ta ce daga lokacin babu shiga ba fita daga jihar, domin ba gwamnati damar tabbatar da matakan dakile cutar coronavirus da ta zama annoba a duniya.

    Tuni gwamnatin Filato ta rufe makarantu a fadin jihar.

    Cutar dai ba ta bulla ba a jihar Filato, amma mutum uku ya kamu da cutar a makwabciyarta Bauchi inda cutar ta fara kama gwamnan jihar.

    Gwamnan Filato Simon Lalong

    Asalin hoton, @simon.bakolalong

  15. Labarai da dumi-dumi, An samu sabbin mutum 23 da suka kamu da coronavirus a Najeriya

    Hukumar da ke hana yaduwar cututtuka masu yaduwa ta Najeriya, NCDC, ta sanar da samun sabbin karin mutum 23 da suka kamu da cutar coronavirus.

    Hukumar a shafinta na Twitter ta ce daga cikin mutanen 23, 9 daga jihar Legas ne, 7 daga Abuja inda 5 suka fito daga jihar Akwa Ibom sai kuma mutum 1 daga jihar Kaduna da 1 daga Bauchi.

    Yanzu haka jumullar 'yan kasar da ke dauke da cutar sun zama 174, mutum biyu suka mutu sannan kuma aka sallami mutum 9.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  16. Hotunan wurin da aka tanada domin masu coronavirus a Kebbi

    An kafa wurin da aka tanada domin killace masu cutar coronavirus a jihar Kebbi a Babban Asibitin Tarayya da ke birnin Kebbi.

    ..

    Asalin hoton, @KBStGovt

    ..

    Asalin hoton, @KBStGovt

  17. Dan Najeriyar da ya rasu a Birtaniya sakamakon coronavirus

    Dr Alfaa Saadu

    Asalin hoton, Twitter

    Ana ci gaba da nuna alhini game da rasuwar wani kwararren likita dan asalin Nigeria, Dr Alfa Sa'adu a sakamakon wannan cuta ta Coronavoirus.

    Dr Alfa Sa'adu ya shafe sama da shekaru arba;in yana aiki da asibitoci a Burtaniya da ma Nigeria.

    Ya rasu ne bayan ya yi jinya ta makonni biyu da wannan cuta ta coronavirus.

    Dr Abdullahi Shehu wanda shi ma babban likita ne a Burtaniya, wanda har sarauniya ta ba shi lambar girma ta MBE, ya ce mutuwar Dr Alfa babbar rashi ne ga mutanen Birtaniya da Najeriya.

  18. An samu raguwar mutanen da ake kashewa a Syria

    An samu gagarumar raguwaryawan fararen hulan da ake kashewa a yakin Syria, dadi mafi kankanta da aka samu a wata daya tun soma yakin kasar shekaru tara.

    Alkalumman watan Maris da aka bayar da rahoto sune mafi kankanta tun soma yakin Syria a 2011.

    Masu fafutika a Syria sun ce mutum 103 aka kashe a Syria – rabinsu an kashe su ne daga hare-hare ta sama na dakarun gwamnati.

    Har yanzu ba a samu bullar coronavirus ba a Idlib, amma cutar ta bulla a Syria, inda gwamnati ta dakatar da wasu ayyukan sojinta.

    Turkiya da Rasha da ke mara wa bangarorin da ke rikici a Syria baya sun mayar da hankali ne kan cutar coronavirus a kasashensu.

    Coronavirus ta fara yin kamari a Syria

    Asalin hoton, Getty Images

  19. An yi wa mutum fiye da 2,000 gwajin coronavirus a Najeriya

    Coronavirus

    Ministan lafiya na Najeriya, Dr Osagie Ohanire ya sanar cewa kawo yanzu an yi wa mutum fiye da 2,000 gwajin cutar coronavirus a kasar.

    Ministan ya bayyana hakan ne yayin wani taron manema labarai ranar Laraba da kwamitin gwamnatin tarayya kan covid-19 ya yi a Abuja.

    Ya zuwa yanzu Najeriya ta samu mutum 151 masu dauke da cutar ta coronavirus, inda jihar Legas da Abuja suke da mutanen da suka fi yawa.

  20. Algeria ta saki fursunoni kimanin 5000

    Kasar Algeria ce kasa a Afirka ta baya-bayan nan da ta yi wa fursunoni afuwa sakamakon cutar coronavirus.

    Shugaba Abdelmadjid Tebboune ya yi wa fursunoni kusan 5,000 da aka yi wa hukuncin zaman gidan yari na watanni 18 ko kasa da haka.

    Kasar Ethiopia ita ma ta 'yanta dubban fursunoni.